Hausa NovelsM SHAKUR NovelsMatan Ko Mazan Hausa Novel

Matan Ko Mazan 36

Sponsored Links

💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫

✍🏻M SHAKUR

EPISODE 3️⃣6️⃣

Huuuuhuuuuuu agyara hanya gafa MAMMI HAJIA tazo mana da kayan mata wey no be juju, ba jazz, ba abacadabara ko suddabaru aciki amma kuma aikinshi yafi yankan wuka, MAMMI HAJIA fa tariga tayi suna awannan harkan dan haka ku garzaya aguje kar ayi baku zaku iya shiga whatsapp group nata ta hanyar danna link din nan.

https://chat.whatsapp.com/L9xdTKd3MXZJRW8zkAMSqH

36
NOTE: akwai school of thought daban daban i read something daban daban kan idda. Ance bari terminate idda, at the same time some sunce sai cikin yazama mutum shine yake terminating idda Soo Allahu A’alam Allah masani, feel free to correct me or shed more light on the issue Allah ya ganarda mu gabaki daya Ameen.

Yadan jima kadan amota kafin ya sauko, Baba Amadu ne yakaishi wani special babban falo na Baba wanda yawanci littafai ne na addini suka cikashi ga blue rug ya rufe ko’ina akasan dakin, zama Nura yayi ahankali kanshi akasa ganin Baba shima akasan yayi filo da wata babban filo haka, shigowa Anty Jams dakin tayi takawo ruwa a tray da cincin da soyayyen naman kaza saikuma kunun aya mai sanyi tawuce tafita, Baba yakalli Nura yace “Bismillah Nura” cikeda girmamawa yadauki ruwa yabude ya tsayaya a cup yakai baki yasha kadan Baba yayi gyaran murya yace “Nura” ahankali Nura yadago kanshi yakalli Baba, Baba yace “dudda nasan kasani but still zan gayamaka dakaina miscarriage din da Hadiza tayi yabata iddan ta! Auren dake tsakaninku yakare!” Baba yayi shiru Nura yasauke kanshi kasa ahankali Baba yace “banbancin ku da wacce akama saki uku shine ita dole saitayi wani aure kafin tasake iya auren mijinta while a case dinku koda yanzu kakeson auren Hadiza sadaki kawai zaka biya a daura muku aure” Baba yayi shiru yana kallon Nura da kanshi ke kasa yace “don’t get me wrong Nura, dakai da Hadiza duka yarana ne, sake aurenta ko rashin yin hakan bazai taba chanza matsayinka awajena ba and everything is your decision to make Nura kai d’ana ne, har yau har gobe har kuma jibi, sannan dagani har Amadu munsan abinda Hadiza ta aikata dan mu mazane dan haka live your life according to your rules and regulation Nura” gyadama Baba kai yayi ahankali nan Baba yakawo wani hira daban dan he don’t wanna make him be uncomfortable idan yanason ya maida Hadiza dakanshi zai furta basai ancemai yafadi ba Nura ba yaro bane yasan har cikin ranshi abinda yakeso kenan amman kuma baida right na nuna hakan. Azahar sukeje sukayi suka dawo gidan Nura zai wuce Mama tace “ai baka isa ba saikaci abinci koma” ba yanda ya iya komawa yayi shinkafa akayi da stew kadan yaci shima dan kada suce yakici sannan yatashi yama su Baba sallama, Mama tace “ka shigo ciki” shiga falon yayi Hadiza na zaune kan kujera tana sanye dawani doguwan rigan atamla red daya mata bala’in kyau hada idanu sukayi dasauri Nura yadauke kai yace “Allah kara sauki Hadiza” yakalli su Amali yace “let’s go kids” dasauri yaran sukai wajen shi suka kakkama hannunshi Aman na karban car key dake hannunshi, bawai basason maman su bane but wannan shakuwan dazaisa yaro yahau kuka shi zaibi Mamanshi ko zai zauna da Mamanshi daga Aman har Amali basu dashi, Amali da tayi but tazo tadaina dataga Mamanta no send her, hawaye Hadiza taji ya cicciko idanunta ahankali tace “Dadyn Amal bazaka barsu su kwana ba anan”? Still Nura yaki kallonta yace “maybe saidai gobe basuzo da kayaba” ga mamakinshi kaman ba Hadiza ba tace “Tom shikenan nagode Allah saka da alkhairi, nagode da komi da komi dakamin a asibiti Allah baka lada” dan dago kanshi Nura yayi just to assure kanshi Hadiza ne just agreed da maganan dayayi tashi daya hardamai godiya ganin itane dai yasa gently yace “u welcome” yama su Mama sallama suka fice su Baba suna rakasu har waje suka shiga mota Baba yadawo cikin gidan.
Da sauri Mama cikeda damuwa irin na mahaifiya tace “Malam ya nuna zai komarda ita?” Daga Baba har Amadu girgizama Mama Kai sukayi hakan yasa ahankali Mama tajuya takoma falo kawai ta sami waje ta zauna tai tagumi dasauri Anty Jams tazo kusada ita tace “Mama menene? Yace zai komar da ita”? Itama Hadizan dake zaune kan kujera tana kallon Mama jira kawai take taji ance yace zai kara aurenta dan Nura nada tausayi, shigowa dakin Baba yayi yakalli Hadizan data bishi da kallo tana zazzaro idanu kana iya ganin yanda gabanta ke faduwa zama Baba yayi ahankali kusada Mama ahankali yace “iddan ki yakare Hadiza!” Yadanyi shiru anatse yace “bazan hanaki yin kasuwancin ki ba amman dai ki kira wayanda zaki kira akwaso kayayyakin shagon adawo dasu kano kina karkashina bazan bari kına tafiye tafiye ko ki koma wani gari dazama ba, zaki iya samin wani shago anan kano akama ki cigaba da kasuwancin har zuwa lokacin da Allah yafito miki da wani mijin dan Nura kwata kwata baiyi maganan sake zama dakeba” yanda Hadiza ke kallon Baba wlh wlh zaka iya zubar mata da hawaye kanta ta nuna lips dinta narawa sosai tanaso tama foto da magana ne but takasa sai kawai tafashe da kuka wanda yafi na ko yaushe cikin kukan tace “Baba a ina zan taba samin miji kaman Nura aduniyan nan?” Cikin tsananin kuka tace “A ina zan taba samin miji kaman Nura aduniyan nan” cikin kuka sosai tana girgiza kai tace “bazan taba samun miji kaman Nura ba aduniya! A ina zan sami miji in this my age 33 dazan shiga as first wife, ko ya yarda zai aureni wani iyaye zasubar saurayin dansu ya auro bazawara mai yara biyu as first wife nashi? Mama Kozan sami miji is either me mata biyu ko uku, I can never get mijin dazamu shimfida foundation na rayuwan aure together like Nura” tayi maganan tana zubewa kasan dakin dumus akasa tana kuka, daga Baba har Mama data buga tagumi kallonta suke kaman TV, Anty Jams kuma kawai tasanya hannu ta rufe fuskanta tana kuka kasa kasa.
Hannuwanta biyu tadaura akanta tana wani kalan kuka tace “Anty Jams and Mama maisa dakuka ganni ina tsinannen akidan feminism din nan bakudau bulala kunmin shegen duka ba, ko kubani factory reset mari dazai dawo dani hayyacina ba, ko ki kira Baba ku fadamai? I was lost a lokacin all I needed was someone strict with irons hands that will put me in my place look at me today my life is messed up Baba yarana” tanuna kofa sannan takai hannunta tadaura saman cikinta tana kallon cikin tace “Baba yaran dana daukesu acikin cikin nan na haifosu duniya basuda emotional connection to me and is all my fault, look at them yanzun nan babansu yana cewa su tafi babu ko musu, ai sunaso su zauna da Mommy basuyiba sun bishi sun tafi because basuda emotional bond dani what kind of a woman am I”? Tafashe da wani kalan kuka harda majina dayasa Mama tafashe da kukan datake rikewa acikinta sosai idanun Amadu ma sunyi jazur Hadiza tabashi tausayi Baba ne idanunshi kyam akanta cikin kuka tace “I used to believe yara damuwa ne! I used to believe providing abinda yara keso shine love not knowing spending quality time dasu, playing with them hugging them and kissing them is real love, my children never miss me but they miss Ummi sabida she’s always with them, ta goyasu yarinyar nan ta goya Amali har nakan mata fada tana batamin yarinya da goyo har Aman Ummi goyawa take, I remember wata rana idan nadawo da wuri banson damuwansu nace ta kwashesu suje garden suyi ball that’s how zata dinga wasa da yaran nan while I provide the ball and other accessories for playground dinsu Ummi is the one dake wasan dasu, Baba na cuci kaina dayawa” tafashe da kuka tace “Nura is my entire life, Nura yabani freedom, yabani opportunity, yabani luxury, yabani love, Baba bazan maka karyaba i know all abubuwan danama bawan Allah nan was wrong but Baba kasan mesa nayi hakan? Yau zan fadamaka gaskiyan daban taba gayama kowaba” Tayi dan shiru tace “Baba all abubuwan danama Nura nayi ne sabida nasan yana sona and he will always tolerate me ya hadiye kome namai, ina ganin cewa kalan son dayakemin bazai taba iya rabuwa dani ba, so I can match him, step on him however and whenever I want kuma bazaimin komiba, I feel I can use him to please my friends, the community and association din damuke ciki ashe hauka nayi Baba ko wayanda nake biyemawa su Zeena bahaka sukema mazajensu ba bakin ciki ne sunga yanda Nuri ke sona saisa sukaci nasaran rabani dashi, nama Hajiya all abubuwan nan babu ko darr araina sabida nasan yana sona, kuma na isa dashi, nabiyewa Zeenah nakaishi kotu sabida nasan yanasona he can not do anything, barinma yanda yasan nasami heart attack, Baba wlh wlh Nura baitabamin komiba, mutum neshi dakeson farinciki na da cigaba na, mutum ne daya tsani ina fushi koya ganni cikin damuwa, Nura can kill for me and die for me, kuna ganin zan taba samin selfless miji like Nura? Zan taba samin mijin da duk kudina bazai kalla ba he will still give me kudin salon, kudin kaya, kudin dinki kudin komi? Duk kudina bai taba cewa muyi sharing bill ba, duk kudina bai hanashi kara bani kyauta an ina zan sami kalan mijin nan”? Tayi maganan tana kuka tace “I tortured Nura, I pushed him har ya zamto gwara yadawo gidan by 1 nadare Ina bacci, Baba I took advantage of that man, took advantage of soyayyan dayakemin, Baba na zageshi is not a big deal for me sabida nasan bazai iyamin komiba yana sona, munafuki, algungumi, makiri, matsiyaci, mahaukaci, and so much more babu wanda ban kira Nura dashi ba Baba, Baba nashiga uku wlh nashigo uku Baba, nazo nakaishi kotu Zeenah ta kara da accusing nashi for molesting me, namai shairi na batamai suna i spoilt his record, Baba koni nasan after komi danayi ban chanchanci Nura ya maidani ba amman kuma wlh wlh bazan iya rayuwa babu shi ba, Baba kaga kashin jikina, bargo, jijiya, jini dakuma tsoka na jikina duka Nura sukeso hatta numfashin danake busawa nake shaka Nura yakeso, Baba tell me how can I live without him? Nura is the world best husband that knows how to pamper and spoils his woman but I ruined him, I fucked up, I messed him up and tarnish his image because of stupid feminism mentality na we are equal nidashi, Baba wlh wlh Baba zaku rasani har lahira idan Nura bai komardani ba, Baba tsoron alhaki bazaima barni nayi wani aure ba dan kowa zan aura nasan sai Allah yasa ya gallazamini azaba wacce tafi wanda nabawa Nuri na sau dubu, Baba kaji tausayina cikin nan was the hope na zai komardani cus Nuri loves children but shima yafita, kai kadaine mahaifina hope dina Baba cus Nura najin maganan ka, yanajin kunyanka, kace ya aureni Baba, zuciyata zara tarwatse na rasa Nuri na, wayyooo Allah na ni Hadiza! Wayyyoo zuciyata na shiga uku, na bani, na lalace, na tagaiyare na ga ukuba, Baba dan kaunar dakakema Annabi Muhammadu SAW kasa Nura ya maidani” Tafashe da kuka majina shabe shabe for the first time Baba yasauke kai daga kallonta shima idanunshi sunyi jaaa but baiyi kukaba amman kowa na dakin harda Amadu tasa kuka.

Kuna ganin Baba yama Nura magana???

But then again! I feel bad and emotional for Hadiza, for ita da kanta ta zauna tai analysis na laifukanta haka dudda ance hali zanen dutse but ina ganin mu jira Muga new Hadiza ne ko Yaya??

Kuna ganin ta chanza ko a’a???

Leave a Reply

Back to top button